Kafofin yada labaran yahudawan sahyoniya sun nakalto dakarun gwagwarmaya a Gaza sun 2 daga cikin sojojin mamaya ya zuwa yanzu tare da jikkatar wasu da dama. Majiyoyin Ibraniyawa sun yi ikirarin cewa akwai yiwuwar batar wasu daga wadanda suka jikkata a harin daya gabata a Gaza
Kafofin yada labaran yahudawan sahyuniya sun bayyana cewa an kashe sojojin gwamnatin kasar 2 tare da jikkata wasu mutane 9 a wani harin roka da aka kai a arewacin zirin Gaza.
Wannan harin ya faru a sa’I daya da lokacin ganawar Netanyahu da Trump
Kafofin yada labarai na yaren yahudanci sun rawaito cewa ana ci gaba da kai harin kan titin Al-Jala da ke birnin Gaza. Kafofin yada labaran sun kuma bayar da rahoton cewa, jiragen sama masu saukar ungulu na soji sun sauka a asibitin Yakhlov kuma suna jigilar sojojin da suka jikkata daga zirin Gaza.
Your Comment